Friday 9 January 2026 - 22:18
Kama Shugaban Kasar Venezuela Barazana Ce Ga Dokokin Kasa da Kasa da Zaman Lafiyar Duniya

Hauza/ A wani jawabi da ya yi, Hujjatul Islam Sayyid Karamat Hussain Ja'afari ya bayyana kamaye shugaban kasar Venezuela, Nicolas Maduro, tare da mai dakinsa da kuma karkatar da su zuwa wata kasa daban a matsayin keta a fili na dokokin kasa da kasa. Ya yi gargadin cewa irin wadannan ayyuka suna barazana ga zaman lafiya, adalci, da amincewar juna a fadin duniya.

A cewar rahoton Ofishin Yada Labaran Hauza, Hujjatul Islam Sayyid Karamat Hussain Shu'ur Ja'afari, babban editan jaridar "Sadaqat" ta kasar Indiya, ya jaddada cewa: Kama shugaban wata kasa mai cin gashin kanta ta hanyar amfani da dakarun soja ko na sirri, sannan a fitar da shi wajen iyakokin kasarsa, ba wai kawai batu ne na siyasa ko tsaro ba; a’a, keta sharuddan da duniya ta amince da su ne na huldar kasa da kasa.

Ya kara da cewa irin wadannan ayyuka na nuna fifita karfi da bindiga akan doka, sannan kuma rashin girmama ikon kowace kasa ne na tafiyar da kanta.

Tags

Your Comment

You are replying to: .
captcha